fidelitybank

Sai Sojoji su fatattaki ƴanbindiga daga dazuka kafin a samu zaman lafiya – Ganduje

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya ce, dole sojoji su fatattaki ƴanbindiga su ƙwace dazukan Najeriya domin kawo ƙarshen rashin tsaro.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ta’aziyar jaje ga Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago bisa rasuwar gomman mutane a sanadiyar gobarar fashewar tanka a jihar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

A wata sanarwa da sakataren watsa labaran jam’iyyar APC na ƙasa, Edwin Olofu ya fitar a ranar Alhamis a Abuja, Ganduje ya ce akwai buƙatar a ƙara ƙaimi, musamman wajen fatattakar ƴanbindiga daga dazukan Najeriya domin kawo ƙarshen yaƙin harkokin ƴanbindiga a ƙasar.

“Hanyar da za a magance wannan matsalar ita ce a ƙwace dazuka saboda ƴanbindigar nan a cikin dazuka suke zama. Me ya sa muka koma muna jira su kawo hari, kafin mu tare su? lokacin da nake gwamna, kira na yi ga gwamnatin tarayya da ta zuba sojoji a dajin Falgore, wanda hakan ya sa aka kafa sansanin horar da sojoji.

“Tun daga lokacin ne aka fatattaki ƴanbindiga daga dajin, kuma Kano ta samu zaman lafiya,” in ji Ganduje.

Da yake mayar da martani, Gwamna Bago ya yi godiya bisa ziyarar jajen, sannan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gyare titin Suleja-Minna domin rage yawaitar haɗura.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp