fidelitybank

Sai na kulle duk wani banki da kantin da ya ki karbar tsofaffin kudi – Gwamnan Ogun

Date:

Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun, ya sake yin barazanar kulle bankuna, shaguna ko manyan kantunan da suka ki karban tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000.

Abiodun ya ce zai yi hulda da duk wani dan kasuwa ko mai bada sabis da ya ki amincewa da tsofaffin takardun a matsayin takardar doka.

Domin cimma hakan, gwamnan ya ce mazauna jihar su kira shi a duk lokacin da wani banki ko babban kanti ya ki amincewa da tsofaffin takardun kudi, yana mai cewa zai rufe cibiyar kasuwanci.

Karanta Wannan: CBN ya umarci Bankuna su karbi tsofaffin kudi

A cikin wani faifan bidiyo da wakilinmu ya gani, Abiodun ya ce: “A yanzu haka ina mika takardar gargadi ga duk wata kasuwa, dan kasuwa, gidan mai, ma’aikacin banki da ke kin tsohuwar takardar naira; idan an sanar da ni, zan yi aiki da ku da cikakkiyar doka.

“ Kotun kolin Najeriya ita ce babbar kotun kasar. Kotun koli ta yanke hukuncin cewa tsofaffin takardun Naira sun ci gaba da zama a kan doka. An mayar da wa’adin zuwa ranar 31 ga Disamba.

“Zan kulle shagon ku idan sun ce mini ba ku karbi tsoffin takardun ba. Duk lokacin da ka ɗauki tsohuwar takardar zuwa bankuna kuma suka ƙi karɓa, kira ni. Zan kulle kofofin irin wadannan bankuna, ciki har da manyan kantuna.

“Kuna jigilar ƙungiyoyi da masu sufuri, kar ku ƙi tsohon kuɗin. Idan ka kai bankin aka ki, zan karba daga hannunka, in kai bankin da kaina,” Abiodun ya bayyana cikin karfi.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp