fidelitybank

Sai na kori Atiku da Ayu daga PDP – Wike

Date:

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya sha alwashin korar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu da wasu shugabannin jam’iyyar daga PDP.

Gwamna Wike ya yi wannan alkawarin ne a wajen kaddamar da aikin titi a karamar hukumar Ikwerre ta jihar Ribas a ranar Alhamis.

Wike ya dora laifin rashin nasarar jam’iyyar PDP a zaben shugaban kasa da aka kammala a kan wadanda ya ce sun ki bin kundin tsarin mulkin PDP. Ya yi alkawarin korar su daga jam’iyyar da fara aikin sake gina ta.

Gwamnan ya bayyana matakin a matsayin “kashi na biyu na yakin.”

A cewarsa: “Wadannan mutane sun bar jam’iyyar mu a 2014-2015, jam’iyyar mu ta sha kashi; sun sake dawowa, jam’iyyar mu ta sake yin rashin nasara.

Karanta Wannan: Asari ya bayyana irin gwamnan da zai gaji Wike

“Sun ruguza jam’iyyarmu. Za mu kore su daga jam’iyyar mu. Ba su da rawar da za su taka a jam’iyyarmu.”

Wike ya kuma caccaki shugabancin jam’iyyar PDP bisa zargin shugaban hukumar zabe mai zaman kanta da rashin bin ka’idojin zabe a lokacin da su (PDP) suka ki bin kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

Ya ci gaba da yin ba’a ga shugabannin jam’iyyar PDP da suka gudanar da zanga-zangar nuna adawa da INEC inda ya bayyana shugabannin jam’iyyar a matsayin “kungiyoyin dalibai”.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp