fidelitybank

Sai na kakkaɓe mugayen Mutane da suka hana ruwa gudu kafin na bar mulki – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya sha alwashin tabbatar da cewa “mugan mutane” ‘yan Najeriya sun fuskanci fushin doka.

Tinubu ya yi gargadin cewa za a gurfanar da miyagu a cikin Najeriya ko a wajen Najeriya.

Shugaban wanda mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya wakilta, ya bayyana haka ne a wajen bikin yaye dalibai na kwas na 17 na hukumar leken asiri a cibiyar nazarin harkokin tsaro da ke Abuja ranar Asabar.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a kasar.

“Idan kai mugun mutum ne, ko kana cikin Najeriya ko a waje kana cikin matsala. Za mu bi ku. Za mu gurfanar da ku a gaban kuliya,” inji shi.

Shima da yake jawabi, Darakta-Janar na DSS, Adeọla Ajayi, ya bayyana cewa Najeriya ba za ta fuskanci matsalar tsaro ba idan har dukkan hukumomin tsaro suka yi aiki tare kamar yadda ya kamata.

Ajayi ya ce, “Tare za mu iya yin nasara. CDS da NSA sun haifar da haɗin kai ta hanyar da ban taɓa gani ba a cikin aikina. Muna bukatar yin aiki tare.

“Abin da muka dauka daga nan shi ne babu wani kalubalen tsaro da zai iya kayar da mu idan muka yi aiki tare.

“Ba da jimawa ba, duk ‘yan Najeriya za su kwana da idanunsu biyu a rufe. Godiya ga shugaban kasa bisa alkiblar da kuke bi a kasar.

“Nagode da nada ni. Ba zan taba kyale ka ba.”

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp