fidelitybank

Sai na kakkaɓe mugayen Mutane da suka hana ruwa gudu kafin na bar mulki – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya sha alwashin tabbatar da cewa “mugan mutane” ‘yan Najeriya sun fuskanci fushin doka.

Tinubu ya yi gargadin cewa za a gurfanar da miyagu a cikin Najeriya ko a wajen Najeriya.

Shugaban wanda mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya wakilta, ya bayyana haka ne a wajen bikin yaye dalibai na kwas na 17 na hukumar leken asiri a cibiyar nazarin harkokin tsaro da ke Abuja ranar Asabar.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a kasar.

“Idan kai mugun mutum ne, ko kana cikin Najeriya ko a waje kana cikin matsala. Za mu bi ku. Za mu gurfanar da ku a gaban kuliya,” inji shi.

Shima da yake jawabi, Darakta-Janar na DSS, Adeọla Ajayi, ya bayyana cewa Najeriya ba za ta fuskanci matsalar tsaro ba idan har dukkan hukumomin tsaro suka yi aiki tare kamar yadda ya kamata.

Ajayi ya ce, “Tare za mu iya yin nasara. CDS da NSA sun haifar da haɗin kai ta hanyar da ban taɓa gani ba a cikin aikina. Muna bukatar yin aiki tare.

“Abin da muka dauka daga nan shi ne babu wani kalubalen tsaro da zai iya kayar da mu idan muka yi aiki tare.

“Ba da jimawa ba, duk ‘yan Najeriya za su kwana da idanunsu biyu a rufe. Godiya ga shugaban kasa bisa alkiblar da kuke bi a kasar.

“Nagode da nada ni. Ba zan taba kyale ka ba.”

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp