Ministan babban birnin Najeriya, Abuja, Nyesom Wike, ya sha alwashin haifar wa gwamnonin PDP matsaloli a jihohinsu idan ba su janye hannunsu daga rikicin siyasar jihar Rivers ba.
Wike ya bayyana haka ne ranar Asabar lokacin da yake jawabi a taron jam’iyyar PDP a jihar Rivers da aka gudanar a birnin Fatakwal.
Mista Wike dai na taƙun saƙa da gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara kan jagorancin jam’iyyar PDP a jihar.
A makon da ya gabata ne dai gwamnonin PDP suka fitar da sanarwa bayan taro, wadda shugabansu – gwamnan Bauchi, Bala Mohammed – ya karanta, inda ya ciki ya ce ƙungiyar gwamnonin PDP ta jaddada goyon bayanta ga gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara.
To sai dai a martanin da ya mayar, Ministan na Abuja ya zargi gwamnonin da yunƙurin ƙwace jam’iyyar daga hanunsa, abin da kuma ya ce ba zai saɓu ba.
“Ina son tabbatar muku cewa, ba wai ba za mu bari wani ya ƙwace PDP daga hannunmu ba ne, a a bari na gaya muku, na ji wasu gwamnoni na cewa za su ƙwace jam’iyyar su bai wa wani, to ina tausaya wa waɗannan gwamnoni, domin zan kunno musu wutar da ba za iya kashe ta ba a jihohinsu”, in ji shi.
“Idan Allah ya wanzar maka zaman lafiya a jiharka, kuma ka ce ba ka buƙatar zaman lafiyar, to duk abin da kake so za ka samu, domin kuwa masu iya magana na cewa kowa ya kwana lafiya shi ya so,” in ji Wike.
Tsohon gwamnan Rivers ya ce saboda gwamnonin na ganin wuyansu ya yi kauri, saboda wasu kuɗin da ya ce sun tara, shi yasa suke ƙoƙarin sa bakinsu a jiharsa, ”To ku shirya ni ma ina da jan wuyan da zan iya yi muku hakan a jihohinku”.