fidelitybank

Sai na baiwa gwamnonin PDP matsala a jihohin su – Wike

Date:

Ministan babban birnin Najeriya, Abuja, Nyesom Wike, ya sha alwashin haifar wa gwamnonin PDP matsaloli a jihohinsu idan ba su janye hannunsu daga rikicin siyasar jihar Rivers ba.

Wike ya bayyana haka ne ranar Asabar lokacin da yake jawabi a taron jam’iyyar PDP a jihar Rivers da aka gudanar a birnin Fatakwal.

Mista Wike dai na taƙun saƙa da gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara kan jagorancin jam’iyyar PDP a jihar.

A makon da ya gabata ne dai gwamnonin PDP suka fitar da sanarwa bayan taro, wadda shugabansu – gwamnan Bauchi, Bala Mohammed – ya karanta, inda ya ciki ya ce ƙungiyar gwamnonin PDP ta jaddada goyon bayanta ga gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara.

To sai dai a martanin da ya mayar, Ministan na Abuja ya zargi gwamnonin da yunƙurin ƙwace jam’iyyar daga hanunsa, abin da kuma ya ce ba zai saɓu ba.

“Ina son tabbatar muku cewa, ba wai ba za mu bari wani ya ƙwace PDP daga hannunmu ba ne, a a bari na gaya muku, na ji wasu gwamnoni na cewa za su ƙwace jam’iyyar su bai wa wani, to ina tausaya wa waɗannan gwamnoni, domin zan kunno musu wutar da ba za iya kashe ta ba a jihohinsu”, in ji shi.

“Idan Allah ya wanzar maka zaman lafiya a jiharka, kuma ka ce ba ka buƙatar zaman lafiyar, to duk abin da kake so za ka samu, domin kuwa masu iya magana na cewa kowa ya kwana lafiya shi ya so,” in ji Wike.

Tsohon gwamnan Rivers ya ce saboda gwamnonin na ganin wuyansu ya yi kauri, saboda wasu kuɗin da ya ce sun tara, shi yasa suke ƙoƙarin sa bakinsu a jiharsa, ”To ku shirya ni ma ina da jan wuyan da zan iya yi muku hakan a jihohinku”.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp