Magatakardar Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Jami’a (JAMB), Farfesa Ishaq Oloyede, a ranar Talata ya ce da zarar an kammala komai na hukumar, za a fitar da sakamakon jarrabawar gama-gari (UTME) 2022 da aka yi zuwa yanzu.
SIYASA NIGERIA ta ruwaito cewa, a cewar Oloyede, JAMB “ba za ta fitar da sakamakon jarabawar ba, har sai mun samu dukkan rahotannin rashin gudanar da jarabawar.
Ba mu da wani dalilin da zai hana mu fitar da sakamakon, amma kuma muna yin wani bincike na cikin gida,” Oloyede ya ce, yayin wani taro da mahukuntan hukumar yi wa kasa hidima (NYSC) a Abuja.
“Daya, ba ma son wannan yanayin da ka fitar da sakamako, kuma ka fara janye wasu; don haka mun nemi mutane da su gabatar da rahotanni, musamman na munanan ayyuka.
“Kuma a rana ta farko bayan an shirya sakamakon, yanzu mun bincika kuma mun ga cewa kusan kashi 40 cikin 100 na rahoton ba sa shigar ba.
“Don haka, me zai sa a saki kashi 60 cikin 100 kuma a haifar da rudani? Mun dage cewa, a bana ba za mu fitar da sakamakon ba har sai mun samu dukkan rahotannin tabarbarewar jarrabawa.”