Dattawan Igbo na barazanar ballewar yankin daga Najeriya idan ba’a basu shugabancin kasar nan ba a 2023.
Manyan masu fada a ji na kabilar, sun lashi takobin hukunta duk dan siyasar Igbo da ya karbi kujeran mataimakin shugaban kasa a cewarsu, kawai a baiwa dan kabilar shugabancin Najeriya, domin ya gyara kasar.
Sannanu kuma masu fada a ji na kabilar Igbo, karkashin kungiyar dattawan kabilar Igbo IECF, sun bayyana cewa, wajibi ne a baiwa yankin kujeran shugaban kasar Najeriya a 2023.
Dattawan sun yi gargadi ga ‘yan siyasar yankin kada wanda ya kuskura ya yarda a dauke shi a matsayin dan takarar kujeran mataimakin shugaban kasa.