fidelitybank

Sai da mu ka bi ƙalidoji wajen mamaye ofishin SERAP – DSS

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi ƙarin haske kan dalilan da suka sa jami’anta suka mamaye ofishin ƙungiyar kare hakkin jama’a da tattalin arzikin ƙasa (SERAP) a Abuja ranar Litinin.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar a yau Talata a shafinta na intanet, ta yi watsi da rahotannin da ke cewa jami’anta sun kai farmaki ofishin SERAP, inda ta ce ziyarar wani ɓangare ne na bincike da ta saba yi.

DSS ɗin ta jaddada cewa ba daidai ba ne misalta abin da jami’an suka yi a matsayin cin zarafi da kuma tsoratarwa.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta cika da tambayoyi da dama dangane da mamaye ofisoshin SERAP da ke Abuja da Legas ba bisa ka’ida ba.”

“Waɗannan bayanan duk ba haka bane ne, kuma idan dai za a iya tunawa, an aike da wata tawaga ta ma’aikatanmu guda biyu bisa doka domin gudanar da bincike na yau da kullum a ofishin SERAP da ke Abuja.”

“Abin takaicin shi ne yadda aka yi kuskuren fassara wannan a matsayin hari da cin zarafi, da kuma tursasa wa jami’an SERAP ba bisa ƙa’ida ba.” in ji sanarwar.

Hukumar ta DSS dai ta buƙaci jama’a da su yi watsi da waɗannan rahotannin da ba su tushe.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp