fidelitybank

Sai da mu ka bi ƙalidoji wajen mamaye ofishin SERAP – DSS

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi ƙarin haske kan dalilan da suka sa jami’anta suka mamaye ofishin ƙungiyar kare hakkin jama’a da tattalin arzikin ƙasa (SERAP) a Abuja ranar Litinin.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar a yau Talata a shafinta na intanet, ta yi watsi da rahotannin da ke cewa jami’anta sun kai farmaki ofishin SERAP, inda ta ce ziyarar wani ɓangare ne na bincike da ta saba yi.

DSS ɗin ta jaddada cewa ba daidai ba ne misalta abin da jami’an suka yi a matsayin cin zarafi da kuma tsoratarwa.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta cika da tambayoyi da dama dangane da mamaye ofisoshin SERAP da ke Abuja da Legas ba bisa ka’ida ba.”

“Waɗannan bayanan duk ba haka bane ne, kuma idan dai za a iya tunawa, an aike da wata tawaga ta ma’aikatanmu guda biyu bisa doka domin gudanar da bincike na yau da kullum a ofishin SERAP da ke Abuja.”

“Abin takaicin shi ne yadda aka yi kuskuren fassara wannan a matsayin hari da cin zarafi, da kuma tursasa wa jami’an SERAP ba bisa ƙa’ida ba.” in ji sanarwar.

Hukumar ta DSS dai ta buƙaci jama’a da su yi watsi da waɗannan rahotannin da ba su tushe.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp