fidelitybank

Sai da Amurka ta yi mana gargadi kafin yin amfani da jirgin yakin Super Tucano – Gwamnati

Date:

Fadar shugaban kasa ta kare matakin ta na jan ƙafa kan tura jirgin yaƙi samfurin Super Tucano, domin yakar barayin daji masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa a Arewa maso Gabashin kasar.

Fadar ta ce, kafin gwamnati ta sayi jiragen yaƙin daga Amurka, akwai yarjejeniyar da aka cimma gabanin cinikin, yadda Najeriya ba za ta faɗa kan laifukan take hakkin ɗan adam ba.

Mai magana da yawun shugaban kan harkar yada labarai, Malam Garba Shehu ne ya sanar da haka a tashar talabijin ta Trust TV.

Garba Shehu na cewa: ”Ana bai wa sojoji horon soji ne, shugaban kasa ya san abin da ya ke yi. Fatan mu da zarar ya kammala aikin nan ya koma gida, kotun manyan laifuka ta duniya ba za ta gayyace shi saboda take hakkin dan adam ba. Don haka mu bar sojoji su yi komai bisa tsari, kuma tsari irin nasu a lokacin da ya dace.

Mallam Garba ya kara da cewa: “Idan kana mu’amala da kasashe kamar Amurka, ya zama dole ka bibiyi ra’ayin jama’a da kare hakkinsu wannan ya na da matukar muhimmanci a gare su. A bayyane ta ke karara, sun sayar wa Najeriya jiragen yaki samfurin Super Tucano, amma ana bin tsarin da dokoki suka tanada wajen tabbatar da hakan.”

“Ka da ku manta tsohuwar gwamnatin Amurka ta Barack Obama ta ki sayar wa Najeriya jiragen yakin saboda zargin take hakkin dan adam, amma shugaba Buhari ya yi kokarin ganin an wanke wannan zargin. Don haka wannan ma za a yi amfani da su a lokacin da ya dace,’‘ in ji Garba Shehu.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp