fidelitybank

Sai da Amurka ta yi mana gargadi kafin yin amfani da jirgin yakin Super Tucano – Gwamnati

Date:

Fadar shugaban kasa ta kare matakin ta na jan ƙafa kan tura jirgin yaƙi samfurin Super Tucano, domin yakar barayin daji masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa a Arewa maso Gabashin kasar.

Fadar ta ce, kafin gwamnati ta sayi jiragen yaƙin daga Amurka, akwai yarjejeniyar da aka cimma gabanin cinikin, yadda Najeriya ba za ta faɗa kan laifukan take hakkin ɗan adam ba.

Mai magana da yawun shugaban kan harkar yada labarai, Malam Garba Shehu ne ya sanar da haka a tashar talabijin ta Trust TV.

Garba Shehu na cewa: ”Ana bai wa sojoji horon soji ne, shugaban kasa ya san abin da ya ke yi. Fatan mu da zarar ya kammala aikin nan ya koma gida, kotun manyan laifuka ta duniya ba za ta gayyace shi saboda take hakkin dan adam ba. Don haka mu bar sojoji su yi komai bisa tsari, kuma tsari irin nasu a lokacin da ya dace.

Mallam Garba ya kara da cewa: “Idan kana mu’amala da kasashe kamar Amurka, ya zama dole ka bibiyi ra’ayin jama’a da kare hakkinsu wannan ya na da matukar muhimmanci a gare su. A bayyane ta ke karara, sun sayar wa Najeriya jiragen yaki samfurin Super Tucano, amma ana bin tsarin da dokoki suka tanada wajen tabbatar da hakan.”

“Ka da ku manta tsohuwar gwamnatin Amurka ta Barack Obama ta ki sayar wa Najeriya jiragen yakin saboda zargin take hakkin dan adam, amma shugaba Buhari ya yi kokarin ganin an wanke wannan zargin. Don haka wannan ma za a yi amfani da su a lokacin da ya dace,’‘ in ji Garba Shehu.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp