Jam’iyyar PDP reshen jihar Legas, ta yi kira ga jami’an tsaro da hukumomin gwamnati da su sa baki cikin gaggawa domin ganin an sako shugabanta Philip Aivoji da aka sace.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP reshen jihar Legas, Hakeem Amode, ya yi wannan kiran nea wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, inda ya ce, An sace Aivoji ne a ranar Alhamis, 25 ga watan Janairu da misalin karfe 6:00 na yamma a hanyar Legas zuwa Ibadan a lokacin da yake dawowa daga taron masu ruwa da tsaki a jihar Oyo da Gwamna Seyi Makinde da Gwamna Ademola Adeleke na Osun.
Ya ce, abin takaici ne yadda garkuwa da mutane ya zama ruwan dare a kasar nan.
Sace Aivoji na nuna matukar bukatar daukar kwararan matakai daga gwamnati da masu ruwa da tsaki don kawar da wannan matsalar.
Ya kara da cewar, suna kira ga gwamnatocin jihohin Oyo, Ogun, da Legas, tare da jami’an tsaro, da su kara kaimi wajen ganin an dawo da shi lafiya ga iyalansa.
Kakakin jam’iyyar PDP ya ce idan aka kara kokarin jami’an tsaro za a ceto Aivoji daga hannun masu garkuwa da mutane.
Rahotanni na cewa ‘yan bindigar sun nemi a biya Naira miliyan 200 kafin su sako shugaban jam’iyyar Phi;ip Aivoji.