fidelitybank

Sai an biya miliyan 200 kafin mu saki shugaban PDP na Legas – ‘Yan bindiga

Date:

Jam’iyyar PDP reshen jihar Legas, ta yi kira ga jami’an tsaro da hukumomin gwamnati da su sa baki cikin gaggawa domin ganin an sako shugabanta Philip Aivoji da aka sace.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP reshen jihar Legas, Hakeem Amode, ya yi wannan kiran nea wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, inda ya ce, An sace Aivoji ne a ranar Alhamis, 25 ga watan Janairu da misalin karfe 6:00 na yamma a hanyar Legas zuwa Ibadan a lokacin da yake dawowa daga taron masu ruwa da tsaki a jihar Oyo da Gwamna Seyi Makinde da Gwamna Ademola Adeleke na Osun.

Ya ce, abin takaici ne yadda garkuwa da mutane ya zama ruwan dare a kasar nan.

Sace Aivoji na nuna matukar bukatar daukar kwararan matakai daga gwamnati da masu ruwa da tsaki don kawar da wannan matsalar.

Ya kara da cewar, suna kira ga gwamnatocin jihohin Oyo, Ogun, da Legas, tare da jami’an tsaro, da su kara kaimi wajen ganin an dawo da shi lafiya ga iyalansa.

Kakakin jam’iyyar PDP ya ce idan aka kara kokarin jami’an tsaro za a ceto Aivoji daga hannun masu garkuwa da mutane.

Rahotanni na cewa ‘yan bindigar sun nemi a biya Naira miliyan 200 kafin su sako shugaban jam’iyyar Phi;ip Aivoji.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp