fidelitybank

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Date:

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded ta Spain, Sadiq Umar da ɗanmajalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kaduna ta arewa, Bello El-Rufai sun haɗa hannu domin mallakar ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna.

Ƙungiyar Rancher Bees, daɗaɗɗiyar ƙungiya ce mai tarihi a jihar Kaduna, da ta yi tashe a arewacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya a shekarun baya, amma sai ta samu koma-baya, har aka daina maganarta.

A wata sanarwa da ya fitar, Sadiq Umar ya bayyana farin cikinsa kan mallakar ƙungiyar, wadda ya ce za su iya ƙoƙarinsu domin dawo da martabarta.

Ya ce, “zan haɗa hannu da Bello El-Rufai domin dawo da martabar ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna. Na taso ina kallon ƙungiyar nan, wadda ta fitar da zaratan ƴanƙwallo da suka yi fice a duniya. Wannan abun farin ciki ne a gare mu,” in ji Sadiq Umar.

Ya ce babban burinsu shi ne ganin ƙungiyar ta koma gasar firimiyar Najeriya, “ina farin cikin irin murnar da na ga magoya bayan ƙungiyar sun fara nunawa da ma mutanen Kaduna. Za mu dawo da harkokin wasa sosai a Kaduna,” in ji Sadiq.

A nasa ɓangaren, Bello El-Rufai ya ce yana farin cikin sa hannu a yunƙurin dawo da martabar ƙungiyar, lamarin da ya ce zai yi iya ƙoƙarinsa domin samun nasara,

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp