fidelitybank

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Date:

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded ta Spain, Sadiq Umar da ɗanmajalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kaduna ta arewa, Bello El-Rufai sun haɗa hannu domin mallakar ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna.

Ƙungiyar Rancher Bees, daɗaɗɗiyar ƙungiya ce mai tarihi a jihar Kaduna, da ta yi tashe a arewacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya a shekarun baya, amma sai ta samu koma-baya, har aka daina maganarta.

A wata sanarwa da ya fitar, Sadiq Umar ya bayyana farin cikinsa kan mallakar ƙungiyar, wadda ya ce za su iya ƙoƙarinsu domin dawo da martabarta.

Ya ce, “zan haɗa hannu da Bello El-Rufai domin dawo da martabar ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna. Na taso ina kallon ƙungiyar nan, wadda ta fitar da zaratan ƴanƙwallo da suka yi fice a duniya. Wannan abun farin ciki ne a gare mu,” in ji Sadiq Umar.

Ya ce babban burinsu shi ne ganin ƙungiyar ta koma gasar firimiyar Najeriya, “ina farin cikin irin murnar da na ga magoya bayan ƙungiyar sun fara nunawa da ma mutanen Kaduna. Za mu dawo da harkokin wasa sosai a Kaduna,” in ji Sadiq.

A nasa ɓangaren, Bello El-Rufai ya ce yana farin cikin sa hannu a yunƙurin dawo da martabar ƙungiyar, lamarin da ya ce zai yi iya ƙoƙarinsa domin samun nasara,

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp