fidelitybank

Sabuwar Gaba: Mali ta dakatar da baiwa ƴan ƙasar Faransa

Date:

Mali ta dakatar da bayar da bisa ga ƴan ƙasar Faransa, a ofishin jakadancinta da ke birnin Paris da kuma ma’aikatar harkokin waje.

Wata sanarwa daga ƙasar ta ce matakin na ramuwar gayya ne, kan ayyana Mali cikin yankunan da ke da hatsarin shiga.

“Mun yi mamakin yadda Faransa ta ayyana Mali a cikin yankunan da ke da hatsarin shiga”.

A farkon makon nan Faransa ta dakatar da bayar da bisa ga ƴan Mali, ta kuma rufe ofishinta na bayar da bisa da ke Bamako babban birnin Mali.

Dambarwa tsakanin ƙasashen biyu ta samo asali ne daga juyin mulkin da sojoji suka yi wa shugaban Nijar Mohamed Bazoum, makonni biyu da suka wuce.

Gwamnatocin mulkin soji a Mali da Burkina Faso da kuma Guinea duk sun bayyana goyon bayan su ga juyin mulkin, kuma sun yi gargaɗi kan ɗaukar matakin soji kan dakarun da suka kifar da gwamnati a Nijar.

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Mali da Faransa bayan dakarun Malin sun yi juyin mulki a 2020 da kuma 2021.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp