Shugaban kwamitin gyare-gyaren haraji na ƙasa, Taiwo Oyedele, ya ce ƙudurin haraji da ke gaban majalisar ƙasar zai zama doka kafin rubu’in farko na shekarar nan ta 2025 na ƙare.
Dokar dai ta ɗauki hankalin mutane ƙasar, lamarin da ya jawo tsaiko wajen tabbatar da shi a majalisar, musamman bayan majalisar tattalin arzikin ƙasar ta buƙaci a dakata.
Sai dai a makon jiya ne ƙungiyar gwamnonin ƙasar ta amince da ƙudurin, amma tare da yin wasu kwaskwarima da ta ce zai magance abubuwan da ake fargaba.
Da yake jawabi a wajen wani taro mai taken The Platform, Oyedele ya ce za a fara amfani da dokar ne a watan Yulin bana.
“Muna sa ran za a amince da ƙudurorin haraji kafin ƙarshen rubu’i na farko na wannan shekarar, inda za mu ba masu biyan haraji lokaci domin su fara shiri kafin ya fara aiki a watan Yuli,” in ji shi, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
A game da cire tallafin man fetur, Oyedele ya ce yana cikin manyan matakai masu muhimmanci da aka ɗauka a Najeriya.