fidelitybank

Sabuwar baraka ta kunno kai tsakanin magoya bayan Tinubu

Date:

Wata sabuwar ɓaraka ta kunno-kai tsakanin magoya bayan ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu, bayan wata kungiyar ƴan APC ma’abota dandalin sada zumunta daga arewacin kasar ta ce ta janye daga tafiyar.

Kungiyar ta ce ta dauki wannan matakin ne bayan ta fahimci cewa take-taken ɗan takarar na nuna cewa ba ya bukatar ƴaƴan nata.

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaɓen Bola Tinubun ya ce zai duba lamarin.

Magoya bayan jam’iyyar ta APC da kuma ɗan takarar shugaban kasar nata da ke karkashin kungiyar mai suna Arewa APC Media Influencers da Ingilishi sun ce sun dau wannan mataki ne bayan sun fahimci cewa ana yi musu riƙon sakainar-kashi.

A cewar su sun yi wa shugaban kasa mai barin gado makauniyar soyayya, inda aka ci yaƙi da su, amma daga karshe aka mai da su karan kada miya.

Matasan na cewa sun koyi darasi ba za su yi tafiyar Tinubu ba sai an yi dalla-dalla da su, in ji Mallam Rabi`u Ali Biyora shugaban kungiyar

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaben Bola Tinubu ya ce ba halin ɗan takarar ba ne watsi da magoya bayan sa, kuma zai bincika.

A Najeriya kusana ana iya cewa da sannu tasirin irin wadannan matasa ma’abota dandalin sada zumunta da aka fi sani da ‘yan soshiyal midiya na karuwa sosai a siyasar kasar.

A yanzu dai ta kai ga wadannan mutane na iya iya sanya soso da sabulu wanke fari ya yi sol, kazalika suna iya mai da fari baki idan aka samu akasi wannan ne ya sa wasu `yan siyasar ke cewa fada da su ba riba. In ji BBC.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp