fidelitybank

Sabuwar baraka ta kunno kai tsakanin magoya bayan Tinubu

Date:

Wata sabuwar ɓaraka ta kunno-kai tsakanin magoya bayan ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu, bayan wata kungiyar ƴan APC ma’abota dandalin sada zumunta daga arewacin kasar ta ce ta janye daga tafiyar.

Kungiyar ta ce ta dauki wannan matakin ne bayan ta fahimci cewa take-taken ɗan takarar na nuna cewa ba ya bukatar ƴaƴan nata.

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaɓen Bola Tinubun ya ce zai duba lamarin.

Magoya bayan jam’iyyar ta APC da kuma ɗan takarar shugaban kasar nata da ke karkashin kungiyar mai suna Arewa APC Media Influencers da Ingilishi sun ce sun dau wannan mataki ne bayan sun fahimci cewa ana yi musu riƙon sakainar-kashi.

A cewar su sun yi wa shugaban kasa mai barin gado makauniyar soyayya, inda aka ci yaƙi da su, amma daga karshe aka mai da su karan kada miya.

Matasan na cewa sun koyi darasi ba za su yi tafiyar Tinubu ba sai an yi dalla-dalla da su, in ji Mallam Rabi`u Ali Biyora shugaban kungiyar

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaben Bola Tinubu ya ce ba halin ɗan takarar ba ne watsi da magoya bayan sa, kuma zai bincika.

A Najeriya kusana ana iya cewa da sannu tasirin irin wadannan matasa ma’abota dandalin sada zumunta da aka fi sani da ‘yan soshiyal midiya na karuwa sosai a siyasar kasar.

A yanzu dai ta kai ga wadannan mutane na iya iya sanya soso da sabulu wanke fari ya yi sol, kazalika suna iya mai da fari baki idan aka samu akasi wannan ne ya sa wasu `yan siyasar ke cewa fada da su ba riba. In ji BBC.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp