Wani Malamin Tattalin Arziki a Jamiāar Tarayya ta Gusau, Dr. Ibrahim Shehu Nadabo, ya jaddada bukatar gaggawa da sake fasalin kudin Najeriya cikin gaggawa kamar yadda Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emefiele ya gabatar.
Nadabo ya bayyana cewa, mutane da dama sun yi wa kan su almundahana, sun tara kudi a dakunansu na kashin kansu, saboda ba za su iya ci gaba da daukar su a banki ba saboda tsoron kada a yi musu tambayoyi daga Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Taāannati (EFCC) da sauran hukumomin yaki da cin hanci da rashawa.
Ya lura cewa da zarar an sake fasalin kudin nan da nan, “ko dai sun fara siyan daloli da kudin, ko kuma su batar da duk abin da suka tara.”
A cewarsa, galibin āyan siyasa sun ki kai wa banki dukiyoyinsu saboda tsoron kada a kama su.
“Saboda haka, idan aka sake fasalin kudin nan take, ko dai su fara yiwa talakawa zagon kasa, su sayi kudaden kasashen waje ko kuma makudan kudaden da ke ajiye a cikin dakunan kwanan su sun zama marasa amfani,” in ji shi.
Ya roki hukumar EFCC, da sauran hukumomin yaki da cin hanci da rashawa da su haska fitilar bincikensu a bankuna da sauran muhimman wurare domin su wadannan attajiran za su fara fitar da dukiyoyinsu da ake zarginsu da yin musaya da dala ko kuma su biya a asusun banki na āyan uwa da abokan arziki.