Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta biya wasu makudan kudade ta fuskar diyya ga mutanen da aikin gina layin dogo na jihar ya shafa.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Lahadin da ta gabata, kamar yadda wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Mista Gboyega Akosile ya fitar, yayin da yake duba ayyukan gine-ginen da ake gudanarwa a kusa da aikin layin Red Line.
Sanwo-Olu, wanda mataimakinsa, Dakta Obafemi Hamzat, da ‘yan majalisar zartarwa suka rattaba hannu a kai ziyarar, ya kara da cewa, kayayyakin sufurin da hukumar kula da zirga-zirgar manyan tituna ta Legas ke ginawa, za su samu karfin jigilar fasinjoji sama da 500,000 a kullum idan zai fara aiki a farkon kwata na 2023.
Ya ce, “Red Line aiki ne da gwamnatinmu ta tsara kuma ta fara, wanda za a gudanar da shi a tsawon rayuwar wannan gwamnati. Mun ba da alkawarin tabbatar da kammala aikin a karshen wannan shekara kamar yadda muka yi alkawari.
“Wannan shi ne ziyarar mu ta hudu na duba wannan aiki a cikin shekarar nan kadai kuma a duk lokacin da muka zo, akwai gagarumin ci gaba da dan kwangilar ke samu a hanyar jirgin kasa.