fidelitybank

Sabon fim din Sharukh Khan ya tayar da kura a Indiya

Date:

An soke haska fim din Shah Rukh Khan da ake kira Patha a garuruwan Indore da Madhya Paradesh.

Ya kamata a haska wannan fim a birnin Sapna Sangeet wanda mutane ke aka samu damar sayan tikiti ta intanet, sai dai lokacin da mutanen suka je kallon fim ɗin sai suka ci karo da masu zanga-zanga.

Akwai ‘yan sanda jibge a wajen ɗakin kallon amma ba za su iya dakatar da masu zanga-zangar ba.

Bayan haka ne masu sinimar suka dakatar da haska fim ɗin da safiyar Laraba. Baya ga wannan an samu ɓullar wata zanga-zanga a kan fim ɗin a garin Gwalior.

Shahrukh Khan ya yi wannan fim ɗin ne bayan shekara huɗu da ya yi nusau a masana’antar.

An saki fim ɗin Pathan a ranar 25 ga watan Janairun a ɗakunan kallo.

Mambobin Bajrang Dal masu kishin addinin Hindu ne suka yi zanga-zanga a kan Pathan a wajen sinimar da aka shirya haska shi a Bengaluru

Sun rika ƙona hoton fim ɗin. Bayan nan, an ƙara wata zanga-zanga irin wannan a Kalburgi, a daren jiya kuma an yi a kofar gidan kallo na Belagavi da ke Karnakata.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp