fidelitybank

Sabon fim din Sharukh Khan Pathaan ya tayar da kura

Date:

Fim din da fitaccen jarumin fina-finan India na Bollywood Shahrukh Khan,ya yi na baya bayan nan wato Pathaan da za a sakI a mako mai zuwa ya zamo abin tattaunawa duba da irin hasashen da ake zai dauki hankali.

Tun bayan da aka saki tallan fim din mutane ke ta magana a akai kasancewa jarumin ya kwana biyu bai fito a fim ba, kamar yadda BBC ta rawaito. Shahrukh Khan, wanda jarumi ne da ake son shi ba a kasarsa ta India ba, har ma da sauran kasashen duniya, ya shafe shekaru hudu bai fito a fim ba sai a 2023. Jarumin mai shekaru 57 da haihuwa, ya fito da karfinsa a wannan karon a fim din Pathaan bayan a baya ya yi fina-finan da ba su yi wani fice ba.

Ana ganin irin abubuwan da suka faru da jarumin a baya kamar batun kama babban dansa Aryan, inda aka tuhumeshi da ta’ammali da kwayoyi ya janyo masa koma a fina-finan da ya yi a lokutan. Sabon fim din sa na Pathaan, ya kunshi manyan jarumai kamar Deepika Padukone da kuma John Abraham.

A yanzu ba a kasar India ba kadai, har ma da wasu kasashen duniya babu zance da ake a game da fina-finan Bollywood kamar fim din Pathaan, mutane jira suke kawai a sake shi. An kiyasta cewa tun da aka saki tallan fim din a makon da ya wuce, mutane miliyan 49 sun kalleshi a shafin YouTube, haka ma a shafin Tiwita ana ta magana a kansa.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari a Æ™auyuka 15 na Zamfara a mako É—aya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huÉ—u ne suke biyan mafi Æ™arancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faÉ—in Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai Æ´aÆ´a tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...
X whatsapp