Gwamna jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel ya bayyana cewa, mayu sun maka gwamnatin jihar a gaban kotu.
Udom ya ce sun maka shi kotu ne, saboda aikin gina wajen bautar Allah na biliyoyin Naira da ake yi, wanda su a ganin su hakan ba daidai bane.
Premium Times ta rawaito cewa, mutane da dama sun soki gina wajen bautar na biliyoyin Naira wanda ke gudana a yanzu haka a Uyo, inda suke ganin kamata ya yi da an yi amfani da kudin wajen magance muhimman abubuwan ci gaba a jihar mai arzikin man fetur.
A wani shirin kai tsaye da ya yi a gidan radiyo da talbijin a ranar Asabar, an jiyo gwamnan ya na cewa: “Dukka mayu sun hadu sun kai ni kotu, cewa muna gina wajen bauta na Kirista. Sun ce su basu yarda da Allah ba. Shari’ar ta na nan a kotu, mun yi nasara a kansu amma sun daukaka kara.”