Mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Aliyu Gusau, wanda a ke shirin tsigewa daga kujerar sa, ya ce, ana yi masa bita-da-ƙulli ne kawai, saboda ya ki bin gwamnan jihar Bello Matawalle zuwa jam’iyyar APC.
Ranar Litinin din nan ne kwamitin da babbar mai shari’a ta jihar ta kafa zai zauna, domin jin bahasin mataimakin gwamnan, game da wasu tuhume-tuhume da ake yi masa.
Sai dai yayin wannan hira da BBC, ya fito fili ya ce, ba zai amsa gayyatar da a ka yi masa ba, domin an saɓa doka wajen bin ka’idar tsige shi, kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya yi tanadi.