fidelitybank

Saboda gogewar Lauya na naɗa shi sabon shugaban EFCC – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Ola Olukoyede a matsayin sabon shugaban babbar hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya wato EFCC.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale, ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Ngelale ya bayyana cewa naɗin Olukoyede, na tsawon shekara hudu ne a matakin farko, amma sai majalisar dattawa ta tabbatar da shi.

Sanarwar ta ce shugabancin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa na ƙasar na samun sauye-sauye cikin ‘yan watannin da suka gabata, tun bayan hawan Bola Tinubu karagar mulki a ranar 29 ga Mayu.

A ranar 14 ga watan Yunin 2023, Bola Tinubu ya dakatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin shugaban hukumar EFCC, kuma har yanzu yana tsare a hannun hukumomi ba tare da an gurfanar da shi gaban shari’a ba.

Sanarwar ta ce Tinubu ya dakatar da Bawa ne “don ba da damar yin ingantaccen bincike kan yadda ya gudanar da aiki lokacin shugabancinsa”.

Matakin ya zo ne bayan zarge-zarge ”masu nauyi” na tozarta mukaminsa, in ji sanarwar.

Daga nan ne shugaban ya umurci daraktan ayyuka na hukumar Abdulkarim Chukkol ya rike shugabanci EFCC a mataki na wucin gadi.

Ngelale ya ce matakin da shugaban kasar ya dauka na nada Olukoyede a matsayin sabon shugaban EFCC ya samo asali ne daga damar da aka ba shi bisa tanadin dokar da ta kafa hukumar EFCC ta 2004, sashe na 2 karamin sashe na 3.

“Ola Olukoyede lauya ne mai gogewa tsawon shekaru sama da 22 a matsayin mai ba da shawara kuma kwararre ne kan gano laifukan damfara da kuma ƙididdige muhimman bayanai don masu mulki.” in ji Ngelale.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp