‘Yan bindiga sun kona matafiya kimanin mutum 42 a karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto.
Matafiyan wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa wurare daban-daban na kasar nan, domin kaucewa matsalar tsaro da ta addabi yankunansu.
Shaidar gani da ido ya tabbatar da cewa lamarin ya afku ne a daren Litinin da misalin karfe 9 na safe. 7 daga cikin matafiyan ne kawai suka tsira, inda su na kwance a asibiti suna karbar magani.
Lamarin ya faru ne a wani kauye mai suna Teke a yankin Gidan Bawa na Karamar Hukumar Sabon Birni. Inda ‘yan bindigar suka bude musu wuta, domin tsayar da motar, wanda hakan ya yi sanadiyar juyawar motar,nan ta ke ta kama da wuta.
Sai dai hukumomin jihar Sokoto basu ce komi ba kan faruwar lamarin, yayin da ayyukan ta’addanci na ‘yan bindigar ke kara ta’azzara musamman a yankin Sabon Birni dake jihar Sokoto da yankin karamar hukumar Shinkafi da ke jihar Zamfara, wanda ko a makon da ya gabata ‘yan bindigar sun shafe kwanaki suna cin-karensu ba-babbaka a hanyar Shinkafin. Inji Leadership.