fidelitybank

Sabon Birni: Yan Bindiga sun budewa motar matafiya wuta

Date:

‘Yan bindiga sun kona matafiya kimanin mutum 42 a karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto.

Matafiyan wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa wurare daban-daban na kasar nan, domin kaucewa matsalar tsaro da ta addabi yankunansu.

Shaidar gani da ido ya tabbatar da cewa lamarin ya afku ne a daren Litinin da misalin karfe 9 na safe. 7 daga cikin matafiyan ne kawai suka tsira, inda su na kwance a asibiti suna karbar magani.

Lamarin ya faru ne a wani kauye mai suna Teke a yankin Gidan Bawa na Karamar Hukumar Sabon Birni. Inda ‘yan bindigar suka bude musu wuta, domin tsayar da motar, wanda hakan ya yi sanadiyar juyawar motar,nan ta ke ta kama da wuta.

Sai dai hukumomin jihar Sokoto basu ce komi ba kan faruwar lamarin, yayin da ayyukan ta’addanci na ‘yan bindigar ke kara ta’azzara musamman a yankin Sabon Birni dake jihar Sokoto da yankin karamar hukumar Shinkafi da ke jihar Zamfara, wanda ko a makon da ya gabata ‘yan bindigar sun shafe kwanaki suna cin-karensu ba-babbaka a hanyar Shinkafin. Inji Leadership.

 

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp