An ɗage shari’ar Mu’azu Magaji wanda aka fi sani da Ɗan Sarauniya zuwa Juma’a 4 ga watan Fabrairun 2022.
A cikin wata sanarwa da magatakardar kotun Majistare da ke Nomansland a Kano, Auwal Muhammad Tudun Wuzurci ya sanya wa hannu, an ɗaga zaman ne saboda yanayi na tsaro.
Ya bayyana cewa a ranar 3 ga wata wadda ita ce asalin ranar da za a yi shari’ar Mu’azu Magaji, a ranar ne za a yi shari’ar Sheikh Abduljabar Nasiru Kabara, kuma jami’an da za su kai Sheikh Abduljabar kotun da ake masa shari’a a Upper Shari’a Court da ke Ƙofar Kudu su ne dai jami’an da za su kai Mu’azu Magaji kotun da za a yi masa shari’a a Nomansland.
Hakan ya sa aka ɗage shari’ar Dan Sarauniya zuwa 4 ga watan Fabrairu da misalin 2:30 na yamma.