Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sallami ministoci biyar tare da naɗa wasu sababbi bakwai da kuma sauya wa goma ma’aikatu.
Wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fitar a shafinta na X, ta nuna cewa ministocin da aka cire su ne;
Sababbin ministocin da aka naɗa;
- Dr Nentawe Yilwatda – Ministan ma’aikatar jinƙai da yaye talauci
- Muhamamd Maigari Dingyaɗi – Minsitan ƙwadago
- Bianca Odinaka Odumegu-Ojukwu – Ƙaramar ministar harkokin waje
- Dr Jumoke Oduwale – Ministar ma’aikatar kasuwanci da zuba jari
- Idi Mukhtar Maiha – Ma’aikatar kusa da dabbobi
- Hon Yusuf Abdullahi Ata – Ƙaramin ministan gidaje da raya birane
- Suwaiba Said Ahmad phD – Ministar Ilimi
-
Waɗanda aka sallama:
1-Barr. Uju-Ken Ohanenye; ma’aikatar harkokin mata
2- Lola Ade-John; ministan harkokin yawon buɗe idanu
3- Farfesa Tahir Mamman; ministan ilimi
4- Abdullahi Muhammad Gwarzo; ƙaramin ministan gidaje da raya birane
5- Dr. Jamila Bio Ibrahim; ministar matasa
Waɗanda aka sauya wa ma’aikatu:
1-Hon Dr. Yusuf Tanko Sununu; ƙaramin ministan ilimi ya koma ƙaramin ministan jinƙai da rage talauci
2- Dr. Morufu Olatunji Alausa; ƙaramin ministan lafiya, ya koma ministan ilimi
3- Barr. Bello Muhammad Goronyo, ƙaramin ministan ruwa da tsafta, ya zama ƙaramin ministan ayyuka
4-Hon. Abubakar Eshiokpekha Momoh, ministan raya Naija Delta, ya koma ma’aikatar raya yankuna (sabuwa)
5- Uba Maigari Ahmadu, ƙaramin ministan ƙarafa ya koma ƙaramin ministan raya yankuna
6- Dr. Doris Uzoka-Anite, ministar masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta koma ƙaramar ministar kuɗi
7- Sen. John Owan Enoh, ministan raya wasanni ya koma ƙaramin ministan kasuwanci da zuba jari (masana’antu)
8- Imaan Sulaiman-Ibrahim, ƙaramar ministar harkokin ‘yansanda ta koma ministar mata
9- Ayodele Olawande, ƙaramin ministan matasa ya koma ministan raya matasa
10-. Dr. Salako Iziaq Adekunle Adeboye, ƙaramin ministan muhalli, ya koma ƙaramin ministan lafiya.