A ƙalla mutum biyar ne suka rasa rayukansu yayin da gommai suka jikkata bayan da aka yi mamakon ruwan sama mai tafe da ƙaƙƙarfar iska da guguwa da birnin Damaturu da ke jihar Yobe a arewa maso gabashin Najeriya.
Jaridar intanet ta Daily Nigerian ta ruwaito hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar ta tabbatar da afkuwar lamarin inda ta ce fiye da gidaje 100 ne suka lalace sakamakon iftila’in.
Sakataren hukumar Mohammed Goje ya ce sun samu labarin lamarin ne daga wasu mutane a jiya Litinin 9 ga watan Mayun 2022, waɗanda suka taimaka wajen gaggawar kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.
Mohammed Goje ya ƙara shaida wa jaridar cewa mutum biyar sun daga cikin 41 da lamarin ya rutsa da su, kuma mutanen sun fito ne daga yankuna daban-daban a birnin na Damaturu, inda aka wuce da su asibiti.
Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da Waziri Ibrahim Extension da Abbari Extension da NayiNawa da Pompomari da rukunin gidajen ‘yan majalisar dokokin jiha da Gujba Road da kuma Maisandari.