Rahotanni sun bayyana cewa, wata babbar mace ta tsallake rijiya da baya a wani gini da ya rufta a lamba 15, titin Oke-Arin, Ilupeju/Palm Grove a jihar Legas.
An bayar da rahoton cewa, ginin mai hawa biyu da aka yi watsi da shi ya ruguje har kasa a safiyar Laraba, 13 ga Yuli, 2022.
An gano cewa, lamarin ya faru ne sakamakon tsufan ginin da ya yi saurin lalacewa.
Sai dai lamarin bai haifar da asarar rai ba sai dai ga wani babban namiji da ya samu kananan raunuka kuma an kai shi asibiti domin kula da lafiyarsa.
Vanguard ta tattaro cewa, an killace ginin da abin ya shafa domin kare duk wata barazana.
Da yake karin haske game da lamarin, Babban Sakatare na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, LASEMA, Dokta Oluwafemi Oke-Osanyintolu ya ce, “Da isarsu wurin da lamarin ya faru, wani bene mai hawa 2 da aka yi watsi da shi ya ruguje babu komai.