fidelitybank

Rusa PDP karamin illa ne ga demokradiyar Najeriya – Sule Lamido

Date:

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya, Sule Lamido, ya yi gargadin cewa ƙoƙarin rusa jam’iyyar tamkar yunƙurin murƙushe dimokaradiyya ne.

Sule Lamido wanda tsohon gwamnan jihar Jigawa ne a arewacin ƙasar kuma tsohon ministan harkokin waje, ya ce ficewar wasu jiga-jigan PDP zuwa APC mai mulki tuggun ne da ba zai yi wa ‘yan siyasa daɗi ba nan gaba.

“Murƙushewa da gana azaba, su ne alamun cewa mulki ya zo – haka abin yake a tarihi,” in ji shi cikin wata hira da BBC.

“Ya kamata a ce Shugaba Bola Tinubu ya yi adalci, ya san cewa shi shugaban kowa da kowa ne, ya ƙyale mu mu ‘yansiyasa mu yi kokawa da APC a jam’iyyance. Amma idan bai yi hankali ba dabarar za ta ci shi.”

A jiya Litinin Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da wanda ya gada Ifeanyi Okowa suka koma jam’iyyar APC a hukumance bayan sun bar PDP.

A baya-bayan nan wasu ‘yanmajalisa daga jam’iyyun adawa na Labour da NNPP sun koma APC ɗin, yayin da ake raɗe-raɗin wasu gwamnonin na kan hanyar komawa APC ɗin.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp