Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya, Sule Lamido, ya yi gargadin cewa ƙoƙarin rusa jam’iyyar tamkar yunƙurin murƙushe dimokaradiyya ne.
Sule Lamido wanda tsohon gwamnan jihar Jigawa ne a arewacin ƙasar kuma tsohon ministan harkokin waje, ya ce ficewar wasu jiga-jigan PDP zuwa APC mai mulki tuggun ne da ba zai yi wa ‘yan siyasa daɗi ba nan gaba.
“Murƙushewa da gana azaba, su ne alamun cewa mulki ya zo – haka abin yake a tarihi,” in ji shi cikin wata hira da BBC.
“Ya kamata a ce Shugaba Bola Tinubu ya yi adalci, ya san cewa shi shugaban kowa da kowa ne, ya ƙyale mu mu ‘yansiyasa mu yi kokawa da APC a jam’iyyance. Amma idan bai yi hankali ba dabarar za ta ci shi.”
A jiya Litinin Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da wanda ya gada Ifeanyi Okowa suka koma jam’iyyar APC a hukumance bayan sun bar PDP.
A baya-bayan nan wasu ‘yanmajalisa daga jam’iyyun adawa na Labour da NNPP sun koma APC ɗin, yayin da ake raɗe-raɗin wasu gwamnonin na kan hanyar komawa APC ɗin.