fidelitybank

Rundunar Ƴan sanda ta gargaɗi kasashen ƙetare a kan tsaro

Date:

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP, Alkali Baba Usman, ya gargadi kasashen ketare kan gargadin ta’addanci a Najeriya.

Usman ya ce ya kamata kasashen ketare su daina sanar da jama’a game da fadakarwar ta’addanci.

Shugaban ‘yan sandan ya ce, sanarwar ta’addancin kwanan nan ya kamata a bai wa ‘yan sanda ba jama’a ba.

Gwamnatocin Amurka da Birtaniya sun fitar da sanarwar tsaro.

A cikin shawarwarin tafiye-tafiye, sun bukaci ‘yan kasar da su kaurace wa Abuja saboda hare-haren da ‘yan ta’adda suka shirya kai wa.

Sun kuma bukaci ‘yan kasar da su fice daga Abuja har sai an magance matsalar ta’addanci.

Sai dai IGP din ya baiwa jama’a tabbacin kare lafiyar su.

IGP ya yi wannan magana ne a ranar Asabar yayin da yake kaddamar da ofishin ‘yan sanda da bariki a Ibusa, karamar hukumar Oshimili ta Arewa a jihar Delta.

Ya ce, “Ta yaya za ku shiga kasar ku ce akwai sanarwar tsaro, ba ku sanar da ’yan sanda ba, kuna zagaya kuna gaya wa mutanen ku; kar ka je Abuja, ka dawo daga Abuja.

“Idan kana da bayanai kan tsaro, ya dace ka sanar da ‘yan sanda kuma za mu nemo hanyar da za mu magance shi, maimakon kai wa jama’a.

“Muna aiki tare da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da tsaron mazauna.”

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp