fidelitybank

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Date:

Rundunar ‘yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar da tattakin nuna goyon baya ga Peter Obi, ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023.

An shirya tattakin ne domin yin bikin murnar cika shekara 64 da haihuwar Mista Obi.

Mai magana da yawun rundunar DSP Mansir Hassan ya ce bayanai sun nuna cewa akwai wasu “miyagu da ke shirin fakewa da gangamin domin haddasa fitina” a jihar.

DSP ya ce rundunar ta dakatar da duk wani taron jama’a mai kama da na siyasa har sai “lokacin da aka fara yaƙin neman zaɓe a hukumance kamar yadda hukumar zaɓe ta ƙasa Inec ta tsara”.

A cewar sanarwar: “Yayin da ake gudanar da zaɓukan fitar da gwani na jam’iyyu a ranar da magoya bayan Obi suka tsara gangamin, rundunar ‘yansandan Kaduna na ganin hakan zai haddasa rikici a wuraren da za a yi zaɓukan, abin da zai jawo rashin doka da oda a jihar.”

Rundunar ta kuma ci alwashin ɗaukar matakin shari’a kan duk wanda ya ƙi bin umarnin dakatar da gangamin siyasar.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp