fidelitybank

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Date:

Rundunar ‘yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar da tattakin nuna goyon baya ga Peter Obi, ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023.

An shirya tattakin ne domin yin bikin murnar cika shekara 64 da haihuwar Mista Obi.

Mai magana da yawun rundunar DSP Mansir Hassan ya ce bayanai sun nuna cewa akwai wasu “miyagu da ke shirin fakewa da gangamin domin haddasa fitina” a jihar.

DSP ya ce rundunar ta dakatar da duk wani taron jama’a mai kama da na siyasa har sai “lokacin da aka fara yaƙin neman zaɓe a hukumance kamar yadda hukumar zaɓe ta ƙasa Inec ta tsara”.

A cewar sanarwar: “Yayin da ake gudanar da zaɓukan fitar da gwani na jam’iyyu a ranar da magoya bayan Obi suka tsara gangamin, rundunar ‘yansandan Kaduna na ganin hakan zai haddasa rikici a wuraren da za a yi zaɓukan, abin da zai jawo rashin doka da oda a jihar.”

Rundunar ta kuma ci alwashin ɗaukar matakin shari’a kan duk wanda ya ƙi bin umarnin dakatar da gangamin siyasar.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp