Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta bayyana damuwarta dangane da wani rahoto mai shafuka 34 na baya-bayan nan da kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta fitar, wanda ya yi zargin jami’an ‘yan sanda da alhakin kashe ‘yan Najeriya da ba su ji ba ba su gani ba a zanga-zangar #EndBadGovernance a watan Agustan 2024.
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International a ranar 28 ga watan Nuwamba ta yi zargin cewa jami’an tsaro sun kashe kimanin ‘yan Najeriya 24, wadanda suka yi zanga-zangar adawa da matsalar tattalin arziki a watan Agusta.
Rahoton ya kuma yi ikirarin cewa kimanin wasu 1,200 da suka hada da kananan yara ‘yan sanda sun kama tare da tsare su a wasu jihohin arewacin kasar.
Da yake mayar da martani, NPF, a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Litinin, ta musanta zargin, inda ta bayyana su a matsayin marasa tushe, da kuma rudani.
Rundunar ta sake nanata cewa a duk tsawon zanga-zangar, ta bi ka’idojin aiki da suka hada da samar da tsaro ga masu zanga-zangar lumana.
Adejobi, ya ce babban sufeton ‘yan sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun “ya jagoranci gudanar da cikakken bincike kan ikirarin. An umarci kwamishinonin ‘yan sanda a jihohin da abin ya shafa su gabatar da cikakkun bayanai kan lamarin cikin mako guda.
“Wannan umarnin yana da nufin gano duk wani sabani daga ka’idojin aiki (SOPs) da ka’idojin aiki, ba tare da la’akari da hukumomin tsaro da abin ya shafa ba”.