fidelitybank

Rundunar ‘yan sanda za ta yi nazari a kan wanda suka zana jarabawa

Date:

Rundunar ‘yan sanda ƙarƙashin jagorancin Babban Sifeto Kayode Egbetokun, ta ce, za ta sake nazarin sunayen mutanen da suka yi nasarar jarrabawar shiga aikin ‘yan sandan ƙasar, wadda hukumar kula da aikin ‘yan sanda ta ƙasar ta shirya.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce jarrabawar ɗaukar sabbin ‘yan sandan cike take ta kura-kurai.

A lokacin da aka saki sunayen ranar 4 ga watan Yuni, shugaban hukumar kula da aikin ‘yan sanda ta ƙasar, Solomon Arase ya ce an bi ƙa’ida wajen tantance mutanen da aka fitar da sunayen nasu.

To sai dai Olumuyiwa Adejobi ya ce da yawa daga cikin sunayen da hukumar ta fiar ba su ma cike takardun neman aikin ba.

Mai magana da yawun rundunar ya ce bayan nazari mai zurfi, kan sunayen da hukumar kula da aikin ɗan sanda ta ƙasarta fitar a shafinta, rundunar ta gano kura-kurai masu yawa kamar haka:.

i) Mafi yawan sunayen ba su ma taɓa cike takardar neman aikin ɗan sanda ba, sannan ba su shiga kowane irin aiki na matakan ɗaukar aikin ba.

ii) Haka kuma wasu sunayen sun ƙunshi jerin mutanen da suka kasa samun nasara a jarrabawar kwamfuta ko suka yi rashin nasara a atisayen motsa jiki.

iii) Akwai kuma waɗanda aka cire kan matsalar lafiya da suke da ita, amma sai aka ga sunayensu cikin jerin sunayen da aka fitar.

vi) Babban abin tayar da hankalin kuma shi ne yadda aka yi zargin amfani da kuɗi ko cin hanci wajen fitar da sunayen, lamarin da ya sa sunayen waɗanda ba su cancanta ba suke fito a jerin.

Kan haka ne Adejobi ya ce babban sifeton ‘yan sandan ƙasar ya rubuta wa shugaban hukumar wasiƙar ƙin amincewa da sunayen, tare da aniyar sake nazarinsu.

Kwanaki shida bayan fitar da sunayen ne, shugaban ƙasar Bola tinubu ya sauke Arase daga muƙamin nasa, tare da maye gurbinsa da Hashimu Argungu, tsohon mataimakin babban sifeton ‘yan sandan ƙasar.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp