Sufeto-Janar na ‘yan sanda ta kasa, Usman Alkali Baba, ya tura manyan jami’an ‘yan sanda domin gudanar da zaben gwamnan jihar Osun da za a yi ranar 16 ga watan Yuli, inda ya yi alkawarin tsaurara matakan tsaro domin gudanar da aikin.
Ya kuma mika kwamishinan ‘yan sandan jihar Osun Olokode Taoheed Olawale zuwa shelkwatar rundunar na wucin gadi har zuwa kammala zabe.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce, mataimakin sufeto-janar na ‘yan sanda mai kula da sashen binciken manyan laifuka na rundunar (FCID), DIG Johnson Babatunde Kokumo ne zai sa ido a zaben.
Wadanda za su taimakawa Kokumo sun hada da mataimakan sufeto-janar na ‘yan sanda hudu, da kwamishinonin ‘yan sanda hudu, da mataimakan kwamishinonin ‘yan sanda 15, da mataimakan kwamishinonin ‘yan sanda 30.
A cewar kakakin rundunar, an kuma tura isassun jami’an ‘yan sanda masu matsayi na manyan Sufetotin ‘yan sanda da kasa domin gudanar da zaben.