fidelitybank

Rundunar tsaro ta NSCDC ta tarwatsa gungun mutane masu karbar cin hanci a zaben Ekiti

Date:

Jami’an tsaron, NSCDC, sun tarwatsa wasu gungun mutanen da ake zargin ana karbar cin hanci a tashar Mobil, daura da makarantar St. Michael da ke unguwar Ajilosun a Ado-Ekiti dake jihar Ekiti.

Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa, NAN, wanda ya sa ido kan yadda za a kada kuri’a a fadin jihar, ya lura da dimbin jama’a da tawagar jami’an NSCDC karkashin jagorancin mukaddashin kwamanda, Haruna Muhammed, ke tarwatsa jama’a.

Mista Musa Faruk, wani mazaunin yankin, ya bayyana cewa wasu da ake zargin ‘yan siyasa ne sun rika raba tsakanin Naira 10,000 zuwa Naira 12,000 ga masu kada kuri’a da suka amince su zabi dan takarar gwamna da suke so.

Ya bayyana cewa a mazabar daya da biyu na ward hudu a St. Michael Nursery and Primary School, da wakilan sun lura da wadanda suka zabe su kafin su ba su kudin.

Wata mai kada kuri’a, Veronica Famigun da ke cikin jama’a, ta ce an dauki tsawon sa’o’i ana siyan kuri’u, inda ta bayyana farin cikinta kan yadda jami’an NSCDC suka tarwatsa wadanda ke yin wannan aika-aika.

Ta kuma jaddada bukatar jami’an tsaro su kara haskaka wasu rumfunan zabe a fadin jihar inda kuma za a iya aikata irin wadannan ayyuka.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan lamarin, Muhammed ya fusata kan barazanar sayen kuri’u da ‘yan siyasa ke yi, inda ya ce mutanensa ba su da wani zabi da ya wuce su tarwatsa masu wannan sana’ar. Ya ce yana da kyau ‘yan kasa su fahimci cewa ya kamata a gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp