fidelitybank

Rundunar tsaro ta NSCDC ta tarwatsa gungun mutane masu karbar cin hanci a zaben Ekiti

Date:

Jami’an tsaron, NSCDC, sun tarwatsa wasu gungun mutanen da ake zargin ana karbar cin hanci a tashar Mobil, daura da makarantar St. Michael da ke unguwar Ajilosun a Ado-Ekiti dake jihar Ekiti.

Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa, NAN, wanda ya sa ido kan yadda za a kada kuri’a a fadin jihar, ya lura da dimbin jama’a da tawagar jami’an NSCDC karkashin jagorancin mukaddashin kwamanda, Haruna Muhammed, ke tarwatsa jama’a.

Mista Musa Faruk, wani mazaunin yankin, ya bayyana cewa wasu da ake zargin ‘yan siyasa ne sun rika raba tsakanin Naira 10,000 zuwa Naira 12,000 ga masu kada kuri’a da suka amince su zabi dan takarar gwamna da suke so.

Ya bayyana cewa a mazabar daya da biyu na ward hudu a St. Michael Nursery and Primary School, da wakilan sun lura da wadanda suka zabe su kafin su ba su kudin.

Wata mai kada kuri’a, Veronica Famigun da ke cikin jama’a, ta ce an dauki tsawon sa’o’i ana siyan kuri’u, inda ta bayyana farin cikinta kan yadda jami’an NSCDC suka tarwatsa wadanda ke yin wannan aika-aika.

Ta kuma jaddada bukatar jami’an tsaro su kara haskaka wasu rumfunan zabe a fadin jihar inda kuma za a iya aikata irin wadannan ayyuka.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan lamarin, Muhammed ya fusata kan barazanar sayen kuri’u da ‘yan siyasa ke yi, inda ya ce mutanensa ba su da wani zabi da ya wuce su tarwatsa masu wannan sana’ar. Ya ce yana da kyau ‘yan kasa su fahimci cewa ya kamata a gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp