fidelitybank

Rundunar Sojin Ƙasa ta yaye sabbin sojoji 4,000

Date:

 

 

Rundunar Sojin Ƙasa ta Nijeriya, wacce a ka fi sani da ‘Nigerian Army’ ta yaye sabbin matasan sojoji guda 4,000.

Da ya ke jawabi a yayin bikin yaye sabbin sojojin, Shugaban Rundunar Sojin Ƙasa, Laftanal Janar Faruk Yahya, ya hore su da su sanya buƙatun ƙasar nan a sama da buƙatunsu na kashin kan su.

Ya kuma yi kira a gare su da su zama masu nuna ƙwarewa da bin ƙa’idar aiki a yayin da su ke aiki.

Shugaban ya yi wannan jawabi ne a yayin bikin yaye sojojin karo na 81 a defo ɗin rundunar sojin ƙasa da ke Zariya, Jihar Kaduna a jiya Asabar.

Da ya ke taya sabbin sojojin murnar kammala horo, Shugaban ya baiyana cewa horon da a ke yiwa sabbin ƙananan sojoji wani cikamaki ne na umarnin shalkwatar sojin ƙasa ta ƙasar nan da ya ke kan doron horo na samar da kwararrun dakarun sojin ƙasa domin cimma ƙudurin kare ƙasar nan.

A wata sanarwa da kakin rundunar ya fitar, Onyema Nwachukwu, Shugaban ya ce bikin yaye sojojin wani gagrumi ne a tarihin horo na rundunar yayin da ta sake horar da sabbin zaƙaƙuran sojoji da za su taimaka wajen kare ƙasar nan.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp