Rundunar sojin Najeriya ta ce. nan gaba za ta miƙa wasu tsoffin ‘yan Boko Haram sama da 500 da ta yaye, hannun hukumomin farar hula, bayan kammala horon raba su da tsauraran ra’ayi.
Ɗaruruwan tsoffin ‘yan Boko Haram ne suka yi rantsuwa a ƙarshen makonan. In ji BBC.
Gwamnatin Najeriya ce, ta ɓullo da shirin wanda sojoji ke gudanarwa a 2015, a wani ɓangare na dabarun yaƙi da ta’addanci.
‘Yan Boko Haram waɗanda bisa raɗin kansu suka ajiye makamai kuma suka miƙa wuya ga hukumomin ƙasar ne ke cin gajiyar wannan shiri na musamman, ciki har da samun horo kan sana’o’in hannu da sauya musu fahimta kan addini.
An ba su tallafin kyautata tunani da nufin sauke su daga tsattsauran ra’ayi, kafin a mayar da su cikin al’umma.
Babban jami’in kula da shirin mai taken ‘Operation Safe Corridor’, Birgediya Janar Joseph Maina ya ce tun bayan fara gudanar da shi, tsoffin ‘yan Boko Haram 1,070 ne tuni aka mayar cikin jama’a.
Da waɗannan tsoffin ‘yan Boko Haram da aka yaye a ƙarshen mako adadin waɗanda suka ci gajiyar horon ya ƙaru zuwa mutum 1,629.
Sai dai har yanzu akwai ɗari-ɗari daga ɓangaren al’umma ga tsoffin ‘yan Boko Haram ɗin, bisa la’akari da irin taɓargazar da ƙungiyarsu ta tafka.
Hukumomin Najeriya sun ce dubban ‘yan Boko Haram ne da iyalansu suka miƙa wuya tun bayan ɓullo da shirin.