fidelitybank

Rundunar soji ta yaye tsofafin ‘yan Boko Haram 500

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce. nan gaba za ta miƙa wasu tsoffin ‘yan Boko Haram sama da 500 da ta yaye, hannun hukumomin farar hula, bayan kammala horon raba su da tsauraran ra’ayi.

Ɗaruruwan tsoffin ‘yan Boko Haram ne suka yi rantsuwa a ƙarshen makonan. In ji BBC.

Gwamnatin Najeriya ce, ta ɓullo da shirin wanda sojoji ke gudanarwa a 2015, a wani ɓangare na dabarun yaƙi da ta’addanci.

‘Yan Boko Haram waɗanda bisa raɗin kansu suka ajiye makamai kuma suka miƙa wuya ga hukumomin ƙasar ne ke cin gajiyar wannan shiri na musamman, ciki har da samun horo kan sana’o’in hannu da sauya musu fahimta kan addini.

An ba su tallafin kyautata tunani da nufin sauke su daga tsattsauran ra’ayi, kafin a mayar da su cikin al’umma.

Babban jami’in kula da shirin mai taken ‘Operation Safe Corridor’, Birgediya Janar Joseph Maina ya ce tun bayan fara gudanar da shi, tsoffin ‘yan Boko Haram 1,070 ne tuni aka mayar cikin jama’a.

Da waɗannan tsoffin ‘yan Boko Haram da aka yaye a ƙarshen mako adadin waɗanda suka ci gajiyar horon ya ƙaru zuwa mutum 1,629.

Sai dai har yanzu akwai ɗari-ɗari daga ɓangaren al’umma ga tsoffin ‘yan Boko Haram ɗin, bisa la’akari da irin taɓargazar da ƙungiyarsu ta tafka.

Hukumomin Najeriya sun ce dubban ‘yan Boko Haram ne da iyalansu suka miƙa wuya tun bayan ɓullo da shirin.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...
X whatsapp