fidelitybank

Rundunar soji ta kama jirgin ruwa dauke da danyen man fetur

Date:

Rundunar Sojin ruwa ta kasa ta ce, rundunarta mai yaƙi satar ɗanyen mai ta yi nasarar kamawa da ƙwace jiragen ruwa na kwale-kwale da ke ɗauke da ɗanyen man Najeriya da aka sace.

Rundunar sojin ruwan ta ce rundunar Dakatar da Ɓarawo mai farautar ɓarayin wadda aka ƙaddamar a farkon Afrilu ta samu nasarori da dama na kama ɓarayin mai a yankin kudu maso kudancin Najeriya mai arzikin fetir.

Sanarwar da rundunar ta fitar ranar Lahadi ta bayyana nasarorin da rundunar ta samu.

Rundunar ta ce jirgin ruwanta na Pathfinder ya kama wasu jiragen ruwa guda tara na Cotonou da ke ɗauke da man dizel a yankin Andoki da Bille a ranar 5 ga Afrilu. Rundunar ta kuma kama man tataccen mai wanda adadinsa ba a tantance ba a yankin Bonny.

An kuma gano wata rijiyar mai da cibiyar da ake tace man girki a Ketoru.Rundunar ta kuma kama wani jirgi ɗauke da ɗanyen mai lita 520,000 da ake zargin sato shi aka yi a yankin Warri.

Rundunar ta ce ta kama tataccen mai na dizel lita 6,000 a yankin Yanagoa na jihar Bayelsa da kuma wasu motocin dakon ko wacce ɗauke da lita 35,000. Ta kuma kama ɗanyen mai lita 50,000 da lita 150,000 da lita 30,000 da ake zargin na sata ne a yankin Warri a ranar 15 ga watan Afrilu.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp