fidelitybank

Rundunar soji ta kama jirgin ruwa dauke da danyen man fetur

Date:

Rundunar Sojin ruwa ta kasa ta ce, rundunarta mai yaƙi satar ɗanyen mai ta yi nasarar kamawa da ƙwace jiragen ruwa na kwale-kwale da ke ɗauke da ɗanyen man Najeriya da aka sace.

Rundunar sojin ruwan ta ce rundunar Dakatar da Ɓarawo mai farautar ɓarayin wadda aka ƙaddamar a farkon Afrilu ta samu nasarori da dama na kama ɓarayin mai a yankin kudu maso kudancin Najeriya mai arzikin fetir.

Sanarwar da rundunar ta fitar ranar Lahadi ta bayyana nasarorin da rundunar ta samu.

Rundunar ta ce jirgin ruwanta na Pathfinder ya kama wasu jiragen ruwa guda tara na Cotonou da ke ɗauke da man dizel a yankin Andoki da Bille a ranar 5 ga Afrilu. Rundunar ta kuma kama man tataccen mai wanda adadinsa ba a tantance ba a yankin Bonny.

An kuma gano wata rijiyar mai da cibiyar da ake tace man girki a Ketoru.Rundunar ta kuma kama wani jirgi ɗauke da ɗanyen mai lita 520,000 da ake zargin sato shi aka yi a yankin Warri.

Rundunar ta ce ta kama tataccen mai na dizel lita 6,000 a yankin Yanagoa na jihar Bayelsa da kuma wasu motocin dakon ko wacce ɗauke da lita 35,000. Ta kuma kama ɗanyen mai lita 50,000 da lita 150,000 da lita 30,000 da ake zargin na sata ne a yankin Warri a ranar 15 ga watan Afrilu.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp