fidelitybank

Rundunar ƴan sanda za ta gudanar da taro na kwanaki 3 a kan zaɓen 2023

Date:

Sufeto Janar na ‘yan sanda na ƙasa, Usman Baba ya amince da gudanar da taro na kwanaki uku ga manyan jami’an ‘yan sanda gabanin babban zabe na 2023.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. Ya ce, taron wani bangare ne na kokarin da rundunar ke yi na tabbatar da zaman lafiya a cikin harkokin tsaron cikin gida da kuma samar da yanayi mai kyau don gudanar da babban zabe a shekarar 2023.

Taron mai taken ‘Muhimmancin tsarin dabarun ‘yan sandan Najeriya don gudanar da zabe cikin lumana’, za a yi shi ne tsakanin ranakun 18 zuwa 21 ga watan Oktoba a Imo.

Sanarwar ta ce, mahalarta taron za su kasance manyan jami’ai masu matsayi na mataimakin sufeto-janar na ‘yan sanda (DIG), mataimakin sufeto-janar na ‘yan sanda (AIG), kwamishinonin ‘yan sanda da sauran shugabannin rundunonin ‘yan sanda.

Ya kara da cewa sauran mahalarta taron za a zabo su a tsanake kan harkokin tsaro da gudanar da zabe a duk fadin duniya, domin su shiga nazari na takwarorinsu da kuma hada ra’ayoyi.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa, za ta tabbatar da gudanar da ingantaccen tsaro kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe da kuma ba da dama ga manyan jami’ai su yi mu’amala da manyan jami’an ‘yan uwa na hukumomin tsaro da INEC da kuma abokan huldar ci gaban kasa da kasa.

Ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai shelanta bude taron tare da gabatar da jawabi. Gwamnoni da hafsoshin tsaro da shugabannin sauran hukumomin tsaro da sufeto-janar na ‘yan sanda na baya wasu baki ne da za su halarci taron.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp