fidelitybank

Rundunar Ƴan sanda ta gargaɗi kasashen ƙetare a kan tsaro

Date:

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP, Alkali Baba Usman, ya gargadi kasashen ketare kan gargadin ta’addanci a Najeriya.

Usman ya ce ya kamata kasashen ketare su daina sanar da jama’a game da fadakarwar ta’addanci.

Shugaban ‘yan sandan ya ce, sanarwar ta’addancin kwanan nan ya kamata a bai wa ‘yan sanda ba jama’a ba.

Gwamnatocin Amurka da Birtaniya sun fitar da sanarwar tsaro.

A cikin shawarwarin tafiye-tafiye, sun bukaci ‘yan kasar da su kaurace wa Abuja saboda hare-haren da ‘yan ta’adda suka shirya kai wa.

Sun kuma bukaci ‘yan kasar da su fice daga Abuja har sai an magance matsalar ta’addanci.

Sai dai IGP din ya baiwa jama’a tabbacin kare lafiyar su.

IGP ya yi wannan magana ne a ranar Asabar yayin da yake kaddamar da ofishin ‘yan sanda da bariki a Ibusa, karamar hukumar Oshimili ta Arewa a jihar Delta.

Ya ce, “Ta yaya za ku shiga kasar ku ce akwai sanarwar tsaro, ba ku sanar da ’yan sanda ba, kuna zagaya kuna gaya wa mutanen ku; kar ka je Abuja, ka dawo daga Abuja.

“Idan kana da bayanai kan tsaro, ya dace ka sanar da ‘yan sanda kuma za mu nemo hanyar da za mu magance shi, maimakon kai wa jama’a.

“Muna aiki tare da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da tsaron mazauna.”

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp