An tsinci gawawwakin yara biyu a baraguzan bandaki da ya ruguje na makarantar firamare ta Burtaniya Bello Memorial da ke Paiko a karamar hukumar Paikoro a jihar Neja.
Har yanzu wakilin Aminiya bai gano abin da yaran ke yi a kusa da ginin da aka ce ya yi rufta ba.
Yayin da wasu majiyoyi suka ce, yaran da suka hada da yaro da wata yarinya suna dirar mikiya tare da abokan aikinsu a kusa da makarantar a lokacin da ginin ya rufta a kansu, inda suka mutu nan take.
Sai dai wasu kuma sun ce, suna diban tarkacen da za su sayar a lokacin da ake gudanar da aikin, suna tona kewayen ginin, ya ruguje.