fidelitybank

Rooney ya zama sabon kocin Birmingham City

Date:

Birmingham City ta nada Wayne Rooney a matakin sabon kociyanta.

Tsohon dan wasan tawagar Ingila, mai shekara 37 ya koma kungiyar da ke buga gasar Championship kan yarjejeniyar kaka uku da rabi.

Rooney ya maye gurbin John Eustace, wanda aka kora ranar Litinin, bayan wata 15 da ya ja ragamar Birmingham.

Wannan shi ne nadin farko da sabon wanda ya mallaki kungiyar dan kasar Amurka mai kamfanin Shelby Comanies Limited ya yi tun bayan da ya karba a watan Yuli.

Rooney zai yi aiki tare da mataimaki, tsohon dan wasan United Ashley Cole, wanda shi ne mataimakin mai horar da matasan Ingila ‘yan kasa da shekaru 21.

Haka kuma John O’Shea shima zai tallafa Rooney, wanda shi ne mai horar da tawagar kwallon kafa ta Jamhuriyar Ireland.

Haka kuma Carl Robinson da Pete Shuttleworth za su yi aiki da Rooney a Birmingham, wadanda suka taimaka masa a DC United.

Wannan shi ne karo na uku da Rooney zai horar da kungiya, bayan kungiyar da take buga MLS da kuma Derby County.

Zai fara jan ragamar wasan farko ranar 21 ga watan Oktoba da zai fuskanci Middlesbrough

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp