Hukumar FA ta Portugal, ta musanta wani rahoto da ke cewa kyaftin din tawagar kasar, Cristiano Ronaldo, ya yi barazanar barin gasar cin kofin duniya.
A cewar Record, Ronaldo ya shaidawa kociyan kungiyar, Fernando Santos, cewa watakila ya tashi daga Qatar bayan ya gano cewa an cire shi ne a karawar da suka yi da Switzerland.
An ce dan wasan mai shekaru 37 ya nutsu daga karshe, ganin tafiyar tasa na iya yin illa ga kungiyar.
Amma Hukumar Kwallon Kafa ta Portugal, a cikin wata sanarwa, ta musanta wadannan ikirari.
A cewar sanarwar: “Labarai da aka fitar a wannan Alhamis sun ruwaito cewa Cristiano Ronaldo ya yi barazanar barin tawagar kasar a wata tattaunawa da Fernando Santos, kocin kasar.
“Hukumar FPF ta fayyace cewa babu wani lokaci da kyaftin din tawagar kasar, Cristiano Ronaldo, ya yi barazanar barin tawagar kasar a lokacin horo a Qatar.”