Mai yaɗa labarai na Burtaniya, Piers Morgan, ya magantu game da rayuwar dan wasan gaba na Al-Nassr, Cristiano Ronaldo a Saudi Arabia.
Tattaunawar da Ronaldo yayi da Morgan ya jawo ficewar sa daga Manchester United a watan Nuwambar bara.
Kyaftin din na Portugal ya soki bangarori da dama na Man United, ciki har da masu mallakarta, kocinta Erik ten Hag da kayayyakin more rayuwa, a cikin hirar.
Sannan Man United ta soke kwantiragin Ronaldo da amincewar juna a watan Nuwamba.
Tun daga nan Ronaldo ya koma kungiyar Al-Nassr ta kasar Saudiyya a matsayin dan wasa kyauta.
Sai dai a cewar Morgan, dan shekaru 37 yana jin dadi sosai a Saudiyya.
“Tabbas (yana farin ciki), na yi musayar ‘yan rubutu tare da shi, kuma yana matukar son su, a ciki da wajen filin wasa,” in ji Morgan.