Cristiano ya fara buga wa Al Nassr gasar Saudi Arabia da kafar dama, bayan da kungiyar ta yi nasarar cin Ettifag 1-0 a ranar Lahadi.
Mai shekara 37, ya koma Al Nassr a watan jiya kan yarjejeniyar da za ta kare a karshen kakar 2025 da zai ke karbar sama da fam miliyan 177 a duk shekara.
Ya buga karawar tun daga farko har aka tashi daga wasan da dan kasar Brazil, Talisca ya ci kwallon a fafatawar.
Da wannan sakamakon Al Nassr tana ta daya a kan teburin babbar gasar tamaula ta Saudi Arabia da tazarar maki daya tsakaninta da Al Hilal.
Ronaldo, wanda ya taka leda a Manchester United da Juventus da Real Madrid – an yi masa tarbar girma daga magoya baya a filin wasa na jami’ar King Saud a Riyadh.
A ranar Alhamis, dan kasar Portugal ya ci kwallo biyu a wasan zakarun Riyadh da Paris St Germain ta yi nasara da ci 5-4.