Kungiyar Al-Nassr na sa ran Cristiano Ronaldo zai isa wannan makon yayin da su ke nazarin yiwuwar siyan Sergio Ramos daga Paris Saint-Germain, in ji Marca.
Ronaldo na dab da kammala wani gagarumin yunkuri na komawa Gabas ta Tsakiya bayan da aka soke kwantiraginsa na Manchester United a watan jiya.
Tare da zuwan dan wasan mai shekaru 37 da haihuwa, kulob din na Saudi Arabiya yana kallon manyan ‘yan wasa a Turai.
Wannan ya hada da N’Golo Kante na Chelsea da daya daga cikin tsoffin abokan wasan Ronaldo, Sergio Ramos.
Kwantiragin Ramos na yanzu da PSG za ta kare a bazara kuma an yi imanin shugaban kulob din Al-Nassr da daraktan wasanni na shirin tafiya Madrid, inda za su ci gaba da yuwuwar cinikin Ramos.
Amma Ronaldo ya ci gaba da zama fifikon kulob din kuma suna sa ran zai koma Saudi Arabiya a ranar 1 ga Janairu.