Rahotonni daga birnin Tel Aviv na Isra’ila na cewa wasu mata biyu sun jikkata sakamakon wasu makaman roka da Hamas ta harba zuwa birnin.
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ambato ma’aikatan lafiya na cewa “An samu harin makaman roka da misalin ƙarfe 2;00 a birnin Tel Aviv, inda makaman suka faɗa wurare biyu a birnin”.
Kungiyar Hamas ta ce hare-haren ramuwar gayya ne kan kisan fararen hula da ake yi a Gaza.
Sojojin Isra’ila sun ce tun ranar 7 ga watan Oktoba an harba makamai kusan 9,500 zuwa cikin Isra’ila, da suka haɗar da rokoki da jirage marasa matuƙa daga Gaza da wasu sassa.
Sojojin sun ce kashi 12 na makaman da aka harba cikin Isra’ila na faɗuwa a cikin yankin Falasɗinawa.