fidelitybank

RMAFC ta wayar da ‘yan Najeriya a kan bambancin albashi da alawus din mu – Femi

Date:

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya yi kira ga Hukumar Tattara Haraji da Kudi, RMAFC, da ta yi la’akari da bayar da karin bayani ga ‘yan Najeriya kan bambancin albashi da alawus-alawus na ‘yan majalisa.

Gbajabiamila ya yi wannan rokon ne a ranar Alhamis a Abuja lokacin da ya karbi bakwancin tawagar RMAFC a majalisar dokokin karkashin jagorancin shugabanta, Alhaji Mohammed Bello Shehu.

Shugaban majalisar ya lura cewa cece-kucen da ake yi kan batun biyan ‘yan majalisar dokoki da mayar da shi muhawara a bainar jama’a a kodayaushe ya samo asali ne, sakamakon dunkulewar albashi da alawus-alawus na ‘yan majalisar tare.

A cewar Gbajabiamila, alawus-alawus na da nasaba da ayyuka ko aiki na ofishin dan majalisa kamar kula da ofishin mazabar, yayin da albashin shi ne ainihin albashin da yake samu a matsayinsa na dan majalisa.

“Ya kamata ku bayyana wa jama’a bambancin albashi da alawus-alawus. Albashi ya bambanta kuma ana nufin alawus don wasu batutuwa masu yawa.

“Wannan bayanin ya kamata ya kasance wani bangare na abin da kuke aiki akai a yanzu game da bangaren shari’a da masu rike da mukaman siyasa”, in ji shi.

Ya kuma shawarci RMAFC da ta gina cibiyar sa ido kan yadda ake tafiyar da harkokin kudaden shiga a dukkan hukumomin da ke samar da kudaden shiga na gwamnati, yayin da ya bukaci ta gabatar da cikakken bayani kan bukatunta domin baiwa majalisar damar yin aiki da ita cikin gaggawa.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp