Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi yayin da sojojin ƙasashen biyu su ka ci gaba da musayar wuta a kan iyakar da ke haɗa su, kwana ɗaya bayan ɓarkewar sabon rikici mai tsanani.
Rahotanni daga hukumomin Thailand na cewa aƙalla mutum 14 – dukkansu fararen hula – ne suka rasa rayukansu a rikicin.
Haka kuma, ɗaruruwan mutane sun jikkata, yayin da dubban mazauna yankunan da ke kusa da iyakar suka tsere domin tsira da rayukansu.
Babban ƙalubalen yanzu shi ne yadda dakarun kowanne bangare ke ci gaba da kai farmaki, lamarin da ke haddasa asara ga ɓangarorin biyu.
A ɓangaren Cambodia kuma, hukumomi sun tabbatar da mutuwar mutum ɗaya a rikicin.
Wannan rikici dai na daga cikin mafi muni da ya taɓa faruwa tsakanin Thailand da Cambodia cikin sama da shekaru goma.