fidelitybank

Rikicin Ukraine: Rasha ta magantu a kan Amurka

Date:

Kasar Rasha ta ce ba ta da kwarin gwiwa bayan tattaunawar farko da Amurka kan rikicin Ukraine, kuma ba za ta bari bukatunta na tabbatar da tsaro daga kasashen Yamma su shiga tsaka mai wuya a tattaunawar ba.

Mai magana da yawun fadar Kremlin, Dmitry Peskov, ya ce, yan a da kyau a ce an gudanar da tattaunawar da aka yi a ranar Litinin a birnin Geneva a fili, mai ma’ana kuma kai tsaye, amma Rasha na da sha’awar samun sakamako kawai.

Kasar Rasha ta tura kasashen yammacin duniya kan teburin tattaunawa ta hanyar tattara sojoji a kusa da kan iyakar kasar ta Ukraine, yayin da ta ke matsa lamba kan wasu bukatu masu nisa da za su hana Ukraine shiga kungiyar tsaro ta NATO da kuma dawo da fadada kawancen shekaru ashirin a Turai.

Amurka ta ce, ba za ta iya amincewa da wadannan bukatu ba, ko da ya ke a shirye ta ke ta shiga cikin wasu bangarori na shawarwarin na Rasha, ta hanyar tattaunawa kan batun tura makamai masu linzami ko iyaka kan yawan atisayen soja.

Sai dai kuma Dimitry Peskov, ya ce lamarin zai kara fitowa fili bayan zagaye na biyu na tattaunawa da Rasha za ta yi a wannan makon tare da kungiyar tsaro ta NATO a Brussels a yau Laraba da kuma kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai (OSCE) a birnin Vienna na kasar Austria ranar Alhamis.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...
X whatsapp