Kasar Rasha ta ce ba ta da kwarin gwiwa bayan tattaunawar farko da Amurka kan rikicin Ukraine, kuma ba za ta bari bukatunta na tabbatar da tsaro daga kasashen Yamma su shiga tsaka mai wuya a tattaunawar ba.
Mai magana da yawun fadar Kremlin, Dmitry Peskov, ya ce, yan a da kyau a ce an gudanar da tattaunawar da aka yi a ranar Litinin a birnin Geneva a fili, mai ma’ana kuma kai tsaye, amma Rasha na da sha’awar samun sakamako kawai.
Kasar Rasha ta tura kasashen yammacin duniya kan teburin tattaunawa ta hanyar tattara sojoji a kusa da kan iyakar kasar ta Ukraine, yayin da ta ke matsa lamba kan wasu bukatu masu nisa da za su hana Ukraine shiga kungiyar tsaro ta NATO da kuma dawo da fadada kawancen shekaru ashirin a Turai.
Amurka ta ce, ba za ta iya amincewa da wadannan bukatu ba, ko da ya ke a shirye ta ke ta shiga cikin wasu bangarori na shawarwarin na Rasha, ta hanyar tattaunawa kan batun tura makamai masu linzami ko iyaka kan yawan atisayen soja.
Sai dai kuma Dimitry Peskov, ya ce lamarin zai kara fitowa fili bayan zagaye na biyu na tattaunawa da Rasha za ta yi a wannan makon tare da kungiyar tsaro ta NATO a Brussels a yau Laraba da kuma kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai (OSCE) a birnin Vienna na kasar Austria ranar Alhamis.