fidelitybank

Rikicin Ukraine: Rasha ta magantu a kan Amurka

Date:

Kasar Rasha ta ce ba ta da kwarin gwiwa bayan tattaunawar farko da Amurka kan rikicin Ukraine, kuma ba za ta bari bukatunta na tabbatar da tsaro daga kasashen Yamma su shiga tsaka mai wuya a tattaunawar ba.

Mai magana da yawun fadar Kremlin, Dmitry Peskov, ya ce, yan a da kyau a ce an gudanar da tattaunawar da aka yi a ranar Litinin a birnin Geneva a fili, mai ma’ana kuma kai tsaye, amma Rasha na da sha’awar samun sakamako kawai.

Kasar Rasha ta tura kasashen yammacin duniya kan teburin tattaunawa ta hanyar tattara sojoji a kusa da kan iyakar kasar ta Ukraine, yayin da ta ke matsa lamba kan wasu bukatu masu nisa da za su hana Ukraine shiga kungiyar tsaro ta NATO da kuma dawo da fadada kawancen shekaru ashirin a Turai.

Amurka ta ce, ba za ta iya amincewa da wadannan bukatu ba, ko da ya ke a shirye ta ke ta shiga cikin wasu bangarori na shawarwarin na Rasha, ta hanyar tattaunawa kan batun tura makamai masu linzami ko iyaka kan yawan atisayen soja.

Sai dai kuma Dimitry Peskov, ya ce lamarin zai kara fitowa fili bayan zagaye na biyu na tattaunawa da Rasha za ta yi a wannan makon tare da kungiyar tsaro ta NATO a Brussels a yau Laraba da kuma kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai (OSCE) a birnin Vienna na kasar Austria ranar Alhamis.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp