Jakadan ƙasar Rasha a Najeriya, Alexei Shebarshin, ya tabbatar wa da gwamnatin tarayya cewa, Rasha ba za ta taɓa ƴan Najeriya ba a rikicin da ke ƙara yin tsanani tsakanin kasar Rasha da Ukraine.
Jaridar Punch ta rawaito cewa, Ministan harkokin kasashen waje, Geoffrey Onyeama, wanda ya samu damar ganawar sirri da jakadan ya shaida wa Shebarshin cewa, Najeriya kawar Rasha ce.
A cewar Onyeama, yayin tattaunawa da Shebarshin, ya sanar da shi cewa, Najeriya ba za ta lamunci cin zarafin ƙasa da ƙasa ba daga wata ƙasar da ke karkashin Majalisar Dinkin Duniya, ƙasar da ke da jakada a Najeriya.
Sai dai Jakadan ya ce, Rasha ba ta kai wa farar hula farmaki, kuma ba za su bari a cutar da Najeriya ba kuma sojojinsu za su tabbatar sun kula. Hasali ma ba sa kai farmakin bangaren farar hula.
“Wannan ne matsayar gwamnatin tarayya kuma muna da ‘yan Najeriya guda 5,600 a Ukraine, kuma hankalin mu a tashe yake, musamman ganin bama-baman da ake aunawa Rasha. Gwamnatin Najeriya ta na shirin zuwa ƙwaso ‘yan kasar”. In ji Onyeama.
A martanin Jakadan Rasha a Ukraine, ya ce, zai yi wa shelkwatar su magana, kuma alamu sun nuna cewa, suna da alaka mai kyau da Najeriya. Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito.